Kamfanin Dillancin Labaran Hauza | Imam Zainul Abidin (A) a cikin ɗaya daga cikin sassan addu'o'in littafin Sahifa Sajjadiyya, yana rokon Allah Madaukakin Sarki kamar haka:
«اللَّهُمَّ ... اجْعَلْ هَمَسَاتِ قُلُوبِنَا، وَ حَرَکَاتِ أَعْضَائِنَا وَ لَمَحَاتِ أَعْیُنِنَا، وَ لَهَجَاتِ أَلْسِنَتِنَا فِی مُوجِبَاتِ ثَوَابِکَ.»
"Ya Ubangiji! Ka sanya wasiwasin cikin zukatanmu, da motsin gabobin jikinmu, da kallon idanunmu, da maganganun harsunanmu, su kasance a cikin abubuwan da suke janyo ladanka.
Ƙarin Bayani:
Domin kaiwa ga matsayin rabo na gaskiya kuma madawwami, lallai ne mutum ya cika dukkan kasancewarsa da soyayya da yardar Ubangiji. Lallai ne cewa mutumtaka mai daraja ta Imam Zainul Abidin (A.S) ta koya mana yadda zamu roki wannan bukata cikin kyawun sauti daga Allah Madaukakin Sarki.
Ya Allah! Duk abin da ke ratsawa ta cikakkiyar zuciyata, Ka sanya shi domin Kai kadai. Ka sanya ni in yi tunani a kanka kuma saboda Kai kadai. Ka karkato da sha'awace-sha'awace da bukatun zuciyata zuwa ga hanyar da ke kawo yardarka.
Ya Allah! Ka sanya dukkan gaɓoɓi da sassan jikina su taka matakai a kan hanyarka da kuma saboda Kai.
Ya Allah! Ka sanya kiftawar idanuna ta kasance domin Kai, domin ganina ya faɗa kawai a kan abin da Kake so.
Kuma ya Allah! Duk abin da ke fita daga harshena Ka sanya shi domin Kai, kada in bude baki in yi magana face don neman yardarka.
Wannan ita ce kololuwar soyayya; cewa mu bukaci dukkan kasancewarmu ta karkata zuwa ga Abun Bauta. Kada mu yi tunani face a kanSa. Kada mu yi aiki face saboda Shi. Kada mu kalli kowa face Shi, kuma kada mu yi magana face saboda Shi; domin kowane abu ya takaitu ne a cikin samuwar Masoyi kuma Abun Bauta, kuma dukkan launuka suna faduwa a gaban launinsa. Lallai cewa "Wanne launi ne ya fi daukaka da fifiko sama da launin Allah?" (Suratul Baqarah: 138).
Mazan jiya sun ce: Ni bawan burin wanda yake karkashin wannan samaniya ne, wanda yake 'yantacce ne daga kowane irin launi na makalewa da abin duniya. (Mawaƙi Hafiz)
Wannan kuma shi ne matsayin ikhlasi (tsarkake niyya).
To, Me Yakamata Mu Yi Domin Kaiwa Ga Wannan Matsayi?
Dole ne a amince cewa kaiwa ga wannan matsayi yana da wahala, amma abu ne mai yiwuwa. Kaiwa ga kowane buri ba zai yiwu ba tare da gwaji da maimaitawa ba. Domin kaiwa ga wannan manufa ta Ubangiji kuma, dole ne mutum ya nema kuma ya yi kokari.
Babban makami kuma hanya ita ce yi wa kai hisabi (muhasabar kai), domin ta wannan hanya ne za a cika kasancewar mutum da hasken Ubangiji mataki-mataki. Kuma lallai cewa yin tarayya da kalaman Ahlul Baiti (A.S) yana ba mutum kwarin gwiwar yin wannan aiki; domin ba zai taba yiwuwa mutum ya zauna da haske ba kuma ya zama shi bai da hasken.
Alamomin Wannan Matsayi
Imam Sadik (A) ya koya mana hanya da alama a cikin wannan babi, domin mu auna kanmu ta hanyarta a cikin tafiyar yi wa kai hisabi.
Yana cewa: "Aiki na gaskiya (mai tare da ikhlasi) shi ne wanda ba ka son kowa ya yabe ka a kansa face Allah Madaukakin Sarki." (Usul al-Kafi, Juzu'i na 2, Shafi na 16).
Kuma yana cewa: "Babu wani bawa da ke kaiwa ga hakikar ikhlasi, har sai ya kasance ba ya son mutane su yabe shi a kan ayyukan da ya yi domin Allah." (Tafsir Majma'ul Bayan).
Saboda haka, duk inda ya kasance har yanzu a cikin tunaninmu da zukatanmu akwai juyo da hankali zuwa ga halitta (mutane) maimakon Mahalicci, wannan yana nufin cewa dole ne mu sake yin ƙoƙari sosai, domin mataki-mataki mu karkatar da dukkan kasancewarmu zuwa ga Masoyi na gaskiya kadai.
Idan abun ya kasance haka, to yabo da jinjinar wasu mutane, ko ma zaginsu da tsangwamarsu, ba za su sami tasiri a cikin ranmu ba; domin a wannan matsayi, mu ba ma ganin kowa face Abun Bauta, kuma ba ma jin wata murya face muryarsa.
Wannan rahoton an tsara shi ne a Sashin Ilimi da Al'adu na Kamfanin Dillancin Labaran Hauzah
Ra'ayinka